Wednesday, July 3, 2019

littafin AGOLA Hausa novels


LITTAFIN AGOLAH!!!


SADAUKARWA!!!
 Zuwaga dukkanin yan uwa da abokan arziki, ina me nuna farincikina gareku, Allah yabar zumunci, ameen.

Bismillahir Rahmanirrahim.

Part 1.....5

Agarin kaduna, cikin unguwar Sarki. Awani katon gida, nashiga domin dauko maku labarin cikin gidan.
    Alhaji Abba Bala, hamshakin me kudine, yanada mata daya da ya,ya biyu mata, Sunan matarshi Hajiya Zarah, takasance yar garin zariya, diyace agurin Malam Garba da matarshi Asabe, kishiyar mamanta, ce, tana kiranta da inna, Asabe takasance mace me kissa, hakan yasa take zaune da Zarah tamkar ita ta haifeta, babu wanda yasan dalilinta nayin haka, talakawa ne acikin danginsu kaf Zarah ce kadai tayi sa,ar auran me kudi, dalilin haduwarsu kuwa lokacin da Alhaji Abba yaje zariya acikin unguwarsu Zarah, yaziyarci wani abokinshi, ahanyarshi ta dawowa yahadu da Zarah tadawo daga aiken da Innarta tayi mata, lokaci guda yaji yakamu da sonta, ahaka. Bayan sungaisa yanemi data nuna mashi gidansu, yayi mata godiya yatafi.

Tundaga ranar soyayya tashiga tsakaninsu, kai tsaye yanemi izinin aurenta agurin mahaifinta, babu bata lokaci ya amshi bukatarshi.
Zarah Allah yayi mata son kudi, babu abinda ta tsana irin talaka, duk da Allah yayita acikinsu amma bata son su, ko taron danginsu akeyi bata shiga, hatta da iyayenta hakuri sukeyi da ita, tasha yin mafarkin ta auri me kudi, segashi Allah ya amsa mata addu,arta tasamu me kudin,
   Zarah bata damu da ilimin addini ba, ko sallah bata damu dayiba, amma tunda suka hadu da Alh, Abba taboye duk wani halinta marar kyau, shi kuma duk farin ciki ya isheshi yasamu diyar gidan mutunci, duk da azahiri iyayenta suna da mutunci amma bata gado suba.

Ahaka akayi aurensu, aka kaita kaduna cikin unguwar sarki akaton gidanta, haka suka cigaba da rayuwarsu cike da so da kauna, hankalinta ya kwanta, arzikin mijinta se karuwa yakeyi, hutu ya zauna mata tuni fatarta, ta murje tayi kyau sosai, tuni ta manta da iyayenta da danginta, tunda akayi bikin bata zuwa garinsu sosai, sede idan mijinta ya matsa mata, shima sede suje tare kuma bazata kwana ba, ko bikin dangine bata cika zuwa ba,  idan ma yabata kudin gudummuwa ko kwatar abunda yabada bata basu, gashi Allah yayi mata rowa.

Ahaka ta haifa mashi diyarta ta farko me suna Hauwa,u sunan mahaifiyarshice yasa dan duk iyayenshi sunrasu, dama shi kadai suka haifa, sede danginshi, hakan yasa aka sama diyarshi sunan mamanshi, ana kiranta da JIDDAH.

Bayan sunanta ne Alhaji Abba yabama Zarah kudi masu yawa yace tafara bussiness, kuma shine yayi mata jagora zuwa dubai domin fara kasuwanci, daga haka harta fara zuwa ita kadai, ahaka ne tahadu da wata mata me suna Hajiya Karima, itama babbar yar kasuwace, halinsu ne yazo daya dan danan suka kulla kawance, itama anan kaduna take. Kawancensu sukeyi sosai, Karima takara nuna ma Zarah duniya anan idonta yakara budewa takara koyon duk wata kissa, sede ita karima bata bin bokaye sede duk wata kissa ta iyata, shiyasa Zarah take zaune da mijinta lafiya, tana yimashi biyayya, saboda yana sakar mata duniya, ita kuma babu abinda takeso kamar kudi, tun bayan haihuwar Jidda taso tayi planing amma Karima tahana ta, acewarta tabari tahaifi namiji.

Bayan shekara biyu da haihuwar Jidda takara haihuwar diyarta mace, har kuka seda tayi, saboda bata samu namiji ba. Ranar suna yarinya taci sunan maman Zarah Saratu, ana kiranta da JALILA.
   Tun daga lokaci Karima tarakata aka tsaida haihuwar acewarta karta tsufa dawuri. Haka yara suka taso cike da kulawa, sudukansu suna da kyau, sede Jalila tafi Jidda kyau, Ahaka suka shiga makaranta, Jidda na P. 1 aka saka Jalila, haka suka cigaba da karatunsu, harsuka girma, alokacin Jidda tana da shekara 18 Jalila tanada 16, alokacin Jidda tana ss 3, Jalila tana ss 1. Halinsu kwata kwata bezo daya ba, Jidda gab daya irin halin Umminsu tadauko, Jalila kuwa irin Halin Dadynsu gareta, tunda suka gama Primary Jidda tafita daga islamiyya, Jalila ce kadai take zuwa, sede Dadynsu besan bata zuwa ba, kasan cewar aiyuka sun mashi yawa, ga tafiye tafiye dayakeyi. Ita kuma umminsu bata damu da ilimin addini ba. Tun Jidda tana ss 1 tafara kula samari, duk wanda zekirata yabata kudi to zata iya binshi duk inda yace, so dayawa Jalila tana kawo kararta amma Umminsu bata daukar maganarta abakin komai, karshema sede takoreta, ahaka harta shiga ss3 alokacin tahadu da kawaye yan duniya tuni suka maida bin maza aikinsu, sede kawarta. Ameera tafisu duniyanci, hakan yasa takaisu asibiti domin suma ayimasu planing. Tun daga lokacin suke sheke ayarsu, kudi suke samu sosai, dayake Jidda tana bama Umminsu kudi hakan yasa tarufe mata baki, takuma zama yar gaban goshinta. Kullum Jalila setayi kuka idan taga halin da yayarta tasa kanta, amma sanin kotayi magana babu wanda ze kulata yasa tayi shiru , saboda Zarah taja mata kunne akan idan har tafada ma Dadynsu wata magana akan Jidda seta tsine mata. Addu,a kawai takeyi mata, sannan ta maida hankalinta akan karatunta na boko dana islamiyya.

Alh. Abba ne yafito cikin shirinshi na tafiya sokkoto. Matarshi da yaranshi biyu, suka rakoshi har bakin mota. Alh, yace to Hajiya nizantafi akula da gida, insha Allah gobe zandawo, kallon yaranshi yayi yace ku kula da karatunku ina fatan babu wata matsala ko? Jidda tayi saurin fadin dady kayan kwalliyarmu sun kare, dariya yayi yace toga dubu 20 nan ai sun isa ko? Karba tayi tana dariya, Jalila tace dady mungode Allah yakara budi. Allah yatsare hanya, sosai yakejin dadin addu,ar da Jalila takeyi mashi aduk sanda yatashi yin tafiya, ita kuwa Jidda tuni tajuya tanufi gida tana murnar samun kudi, daga nesa take fadin dady seka dawo ayo mana tsaraba. Murmushi yayi ya girgiza kanshi yace toni zan wuce, Zarah ta rungumeshi tana fadin seka dawo mijina, Ganin haka yasa Jalila tayi mashi sallam itama ta juya, kiss yayi mata agoshinta yana kara rungumeta, anan yakara mata bandir guda na 1k yace kozata nemi wani abu kafin yadawo. Godiya tayi mashi sannan yashiga motarshi yawuce.

Dayake tafiyar batayi mashi sauri ba, kasancewar tsaye tsaye dayayi kuma dama befito gida dawuru ba, hakan yasa beshiga sokkoto dawuriba segurin karfe 8 na dare, kaitsaye yawuce gurin wadda yazo, dan agobe yakeso yakoma, shiyasa seda yaje yagama abinda yakawoshi sannan yawuce masaukinshi, misalin karfe 9: 30, dayake awajen gari masaukin nashi yake, yafito daga cikin gari tun daga nesa yaga kamar ana tsaidashi, sede beda niyar tsayawa, dan yasan halin yan, fashi babu abinda basayi inde suna son sutareka, haryawuce yaga kamar mata guda biyu ne abikin titin wadanda suke tsaidashi, gani yayi sunata waigen bayansu gashi daya daga cikinsu ta tsugunna kasa kamar tana kuka ganin yawucesu.
    Cikin sauri ya taka burki yakoma baya, suna ganin ya tsaya da gudu daya takama hannun dayar suka nufi gurinshi, tambayarsu yafarayi, amma cike dasauri suka bude bayan motar suka shige. Dakyar take magana, dan Allah bawan Allah katemakemu kayi nisa damu daga gurin nan, wlh sunbiyo mu zasu kashemu...... Ai dajin haka yatada mota yafisgeta suka bar gurin, lokacin damasu binsu suka iso ko alamarsu basu gani ba, haka sukaita dube dubensu, ganin dare nayi suka juya domin komawa gurin Ogansu.

Urs
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/6, 6:12 AM] YAYA HAYAT: ???????????? AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Part 5.....10

 Parking yayi adede wani karamin gida, inda yakasance masauki agareshi aduk lokacin dayazo sakkoto, fita yayi suma suka, fito, tsayawa sukayi suna kallonshi, ahankali yace bansan ina zan kaiku ba, kuma gashi dare yayi, duk da kunce infitar daku wajen gari, agaskiya bazan iya kaiku ba, saboda dare yayi kuma gashi ku mata ne, idan harkun yarda dani kushigo ciki ku kwana idan Allah ya kaimu gobe semusan abinyi, domin nima ba,a garin nan nake ba, wani aiki yakawoni yau, kuma nagama gobe zankoma kaduna acan nake da iyalina.

Kallonshi babbar ciki tayi nawani lokaci sannan tace bakomai munyarda da kai. Bude masu gidan yayi bayan sunshiga yakoma yakwaso kayan cikin motar daya siyo, yashigo ya kulle gidan, zaune suke afalo, shima zama yayi sannan yace. Ga dukkan alamu kuna dauke da yunwa, sede abinci beda yawa kaza ce da lemu nasiyo se biredi, kucinye kawai gobe idan nafita nasamo mana abinda zamu karya dashi, matar tace mungode sosai, amma yanzu abinda kedamuna bamuyi sallar magriba da isha,i ba, murmushi yayi yajinjina irin addini na wannan matar, daganinsu kasan suna tare da yunwa, amma duk da haka take maganar sallah.
      Dakinshi ya nuna masu yace akwai bandaki aciki idan sungama ga abin sallah nan, bayan sunshiga shi kuma yazauna afalo yana tunaninsu, yakosa sugama abinda sukeyi ya tambayesu labarinsu.

Babbar matar takalli yarinyar dasuke tare, da alama diyarta ce saboda tsanin kamar dasukeyi, tace kishiga ciki kiyi wanka sannan kiyo alwala, zama tayi tajirata, har tagama tafito sanye da kayan data cire, daukar hijabinta tayi ta kabbara sallah,ita kuma uwar tashiga domin yin wanka.

     Motsi yaji yasashi saurin dagowa, ganinsu yayi sunfito tsaf dasu, anan take ya iya hango kyawun dake tare dasu, duk da akwai alamun walaha atare dasu hakan be hana kyawunsu fitowa ba, musamman dasukayi wanka suka fita daga cikin dattin dasuke, duk da basu canja kaya ba.

Abinci yadauko masu yamika masu lemu da ruwa harda biredin, murmushi babbar tayi tace da alama kaima bakaci komai ba, kuma gashi kabamu duka, kadebi kazar semu hada biredin, yace a,a kude kuci ku koshi tace Allah bazamu iya cinyewa ba, bata jira abinda zece ba, ta deba mashi kazar dan tana da girma ta mika mashi da biredin, amsa yayi yana mata godiya, murmushi kawai tayi takoma kusa da diyarta suka fara cin tasu, shide ci kawai yakeyi amma hankalinshi yana kan wannan matar, addu,a kawai yakeyi acikin ranshi Allah yasa bata da miji, dan tunda tafito yaji wani irin yanayi akanta.

Bayan sungama takwashe kayan tasa aleda ta kaisu cikin dustbin tasaka, kalon diyarta tayi taga tana gyangyadi, Alh, yace yan mata bacci kikeji kije ki kwanta, murmushi tayi tace to Dady, sosai yaji dadin yanda takirashi da dady, tashi tayi tamasu seda safe tashige daki, matar tace Alhaji kai kuma a ina zaka kwana? Murmushi yayi yace bakomai anan ma ya isheni, zama tayi akasa tayi kasa da kanta tana wasa da yatsunta.

Shima kasa yasauko dan nesa da ita kadan, yace duk da bansan sunanku ba, daga ke har diyarki kiyi hakuri kifadamun labarinku dan bazan iyayin bacci ba idan har banji dalilin dayasa akeso akasheku ba. Idan har babu damuwa inasonjin labarinku, dan Allah.

Hawayen dake idonta ta goge tace tabbas Alhaji ka cancanci kaji labarinmu, domin katemakemu kuma nayarda da kai.
    Nide sunana HAJARA amma anfi kirana da HAJJO kasancewar mudin fulanine, Wannan kuma diyata ce sunanta FALAK, kuma ita kadai Allah yabani, mijina Allah yayi mashi rasuwa yau wata 5 kenan. Ajiyar zuciya yayi aranshi yana fadin Alhamdulillah.

Asalin labarin HAJJO...............
    Ita kadai Allah yabama iyayenta, kuma su fulanin daji ne, basu da taka maiman garin zama, ako da yaushe suna. Canza gurin zama daga wannan guri zuwa wannan, tun bayan auren Baffanta da Innarta suka bar garinsu wanda yake acikin niger, dan sunkasance fulanin niger, haka suka rika yawo gari gari tare da Shanunsu, duk inda sukaje sukan kafa bukkarsu agurin suzauna har zuwa wani lokaci, idan sun gama sesu tashi zuwa wani gari, acikin haka har suka haifi Hajjo, wanda sunan innar Baffantane aka samata.

Lokacin da Hajjo tayi girma har takai sheakara 10 alokacin suka yada Zango acikin garin gusau, acan bayan gari suka kafa bukkarsu tare da wasu yan uwansu fulani dasuka hadu ahanya, koda sukaje gurin sunsami fulani dayawa agurin, anan Baffa yaji dadi, dan tunda suke yawo basu taba haduwa da fulani dayawa kamar wannan ba, anan suka zauna suka cigaba da kiwonsu, inda Inna yakeyin fura da nono tana dora ma Hajjo tana bin sauran sa,anninta zuwa cikin gari sukai talla.
      Baffa dakanshi yayi sha,awar saka Hajjo makarantar boko kasancewar yaga wasu daga cikin yaran gurinsu suna zuwa, ahaka wani abokinshi jauro yayi mashi jagora zuwa makarantar da diyarshi take, shima yasaka Hajjo.

    Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya gwanin dadi, su Hajjo suna zuwa makaranta, ranar da babu karatu kuma sutafi cikin gari talla.

Ahaka harsuka gama primary alokacin Hajjo tana da shekara 16, kyawunta yakara fitowa sosai, kowa sonta yakeyi, watarana suntafi kasuwa ita da kawayenta domin aranar kasuwa takeci, sunje kai talla
    Tunda sukaje kasuwar ta lura dawani yanata kallonta, ahaka harsuka saida suka siyi abinda zasu siya suna shirin tafiya gida. Sallama taji anyi mata, amsawa tayi tare da juyawa domin ganin me mata sallama, wannan wanda tagani yana kallonta shine de tare da abokinshi.

Sannunku yanmata yace yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi, bayan sun gaisa yake tambayarta sunanta, tace Hajjo, murmushi yayi yace Hajara kenan, amma sunan akwai dadi, ni sunana Bashir, kuma ni dan sakkoto ne, ina zuwa nan duk ranar kasuwa, amma Allah betaba jadamu ba, se yau, murmushi tayi tace zanwuce abokan tafiyana suna kirana kada dare yayi, kallon abokinshi yayi yace to abokina nima tafiya zanyi dan banason dare yayi saboda barayin hanya, dan Allah kabisu Hajjo kaganemun gidansu idan nadawo sati mezuwa kwana zanyi seka rakani. Godiya yayi masu sukayi sallama.

Tundaga wannan lokacin soyayya tashiga tsakanin Bashir da Hajjo, har iyayenta sun san dashi,  Baffane yace ma Hajjo idan Bashir yazo yanason ganinshi.

    Zaune suke abisa tabarma, anan Baffa yake tambayar Bashir asalinshi, Yace nide sunana Bashir, kuma ni dan asalin sakkoto ne, iyayena sun rasu tun ina dan shekara 20, banida kowa se kawuna, agurinshi nake kuma gida daya muke dashi, kasuwanci shine sana,ata ina zuwa garuruwa kasuwanci, kuma a sakkoto gidana yake wanda mahaifina ya mutu yabarmun.
    Baffa yace Alhamdulillahi, anan shima yafadamashi alabarinsu, sannan yace tunda naganka naji hankalina ya kwanta da kai, kuma nabaka Hajjo, ko yaushe kake so adaura maku aure zaka iya zuwa, sede inaso dan Allah karike mana Hajjo bisa gaskiya da amana, ita kadai Allah yabamu, kuma kaga bamuda kowa anan, gashi ba gari daya zamu zauna ba, kasan mudin makiyaya ne, inaso karike mani ita, kuma dan Allah karika kawo mana ita duk sanda zaka zo kasuwa, kafin mutashi daga nan, duk da gaskiya bayanzu zamu tashi ba, dan naji dadin zaman gurin nan.

Bashir yace insha Allahu Baffa zaka sameni me riko da amanar daka bani, kuma insha Allah sati mezuwa tare da kawuna zamuzo se adaura mana aure, banaso ku wahalar da kanku, Hajjo kadai nake so, saboda haka kada kusiyi komai. Godiya Baffa yayi mashi sannan yatashi yakira mashi Hajjo.


Bayan sati guda Bashir yazo da kawunshi Wanda yake kanin mahaifinshi dasuke uba daya, sunanshi Lado, amma mutanan gari suna kiranshi da Figo. Kasancewarshi cikenken dan duniya, danshi haryanzu beyi aure ba,sede lalata yaran gari, beda wata sana,ar data wuce shaye shaye da sata, shine oga acikin group dinsu, dan har yara gareshi. Bashir hakuri kawai yake dashi, tunda agida daya suke, sede shi kawu Figo adayan part din yake.

Bayan andaura aure aka shirya Hajjo cikin dinkunan da Bashir yakawo mata, sosai tayi kyau ahaka sukayi sallama da iyayenta suna kuka tafito, kawayenta suka rakota, harbakin mota suka kaita, suma kukan sukeyi ahaka suka tafi, ita kada abaya Bashir da kawu agaba, Bashir ke tuka motar. Tunda Kawu yaganta yake hadiye miyau yana murmushi aranshi yana fadin tsuntsu daga sama gasashshe.

Bayan sunje gida ya aje kawu sukuma suka shige gidan, gidan yayi kyau sosai, komai yasaka aciki kayan more rayuwa masu kyau yasa mata.

Ahaka sukaji gaba da rayuwarsu cike da so da kauna, komai najin dadi Bashir yanayi mata, sosai yake taka tsan tsan da gidanshi, saboda kawu, dan yafikowa sanin halinshi, ko abincin da Hajjo take bashi be bari takai mashi shine yake bashi da kanshi, idan kuma tafiya takamashi sede yakai Hajjo gidan abokinshi Saddik ta kwana, duk yanda kawu yaso kebewa da Hajjo Bashir yahana, idan yashigo gidan sede idan Bashir yana nan. Duk sanda zeje gusau cin kasuwa tare da Hajjo yake zuwa, sosai Hajjo tayi kyau, takara girma.

Bayan shekara biyu da aurensu tahaifi diyarta me kama da ita sede Allah yayima yarinyar kyau sosai, tun tana jaririya, ranar suna Bashir yasa mata FALAK, dan yace yana son sunan sosai.

Tunda FALAK ta girma yasata a primary, ranar dazeje gusau tare suka tafi, kwnansu 2 sannan sukafara shirin dawowa, Inna tadauko wasu awarwaro masu kyau guda biyu ta bama Falak, kasancewar sun mata yawa yasa Hajjo ta amsa tasaka a hannunta, haka taji kamar karsu tafi, Baffa yakara tunama Bashir akan rikon amanar daya bashi, haka sukayi sallama suka tafi.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/6, 1:17 PM] YAYA HAYAT: ????????????AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Part 10.....15

Ahaka rayuwarsu taci gaba da tafiya, Falak tagama primary tashiga secondary school, kyawunta sekara fitowa yakeyi, Hajjo har tsoro takeyi idan Falak zata fita, shiyasa bata barinta zuwa ko ina daga makarantar boko seta islamiyya, haryanzu Kawu besamu damar biyan bukatarshi ba, sede ya matsa ma Bashir lamba akoda yaushe cikin karbar kudi yake, da Bashir yabashi jari zecinyesu, yakuma dawowa, tunda yaga Falak tafara girma kwadayinshi yakoma kanta, sede yakasa samun hanya.

Lokacin da Falak tagama Jss 3 suka shirya domin zuwa ganin gida, tare da Bashir suka tafi amotarshi.
   Mamaki ne yakamsu lokacin dasuka isa bukkokinsu Baffa, babu komai agurin, yakoma fili, kasar gurin duk tayi baki. Kuka Hajjo tafarayi Bashir yanata lallashinta, haka yajuya yanufi cikin gari gurin abokinshi.

   Bayan sungama gaisawa abokinshi yace ai wata rana ne da dare yan fashi suka sauka a bukkokinsu Baffa, suka kwashe masu Shanunsu da duk wasu dukiyarsu, sannan suka tarasu aguri guda suka samasu wuta, babu wanda ya tsira acikinsu.

   Kuka sosai Hajjo da Falak sukeyi, Bashir ma duk dauriyar shi seda yayi kuka, sosai ya tausaya ma Hajjo, ahaka yayi ma abokinshi sallama suka juya, tunda sukaje gida yake aikin lallashin Hajjo, kuma yayi mata alkawarin bazatayi kuka dashi ba, da haka yasamu ta hakura.
    Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya, arzikin Bashir se kara habaka yakeyi, dan yanzu yadena zuwa gusau Lagos kadai yake zuwa, tunda suka Haifi Falak basu kara samun haihuwa ba, Hajjo taso suje asibiti amma Bashir yace a,a haihuwa ta Allah ce tunda sun samu daya ma ai sungode.

    Falak tana ss 2 ayanzu, bangaren islamiyya kuwa gab take da saukewa
 Awannan lokaci tana da shekara 16, takara zama budurwa, komai natana yafito, hakan yasa iyayenta suka kara saka matakan tsaro akanta, dan kawu yace arika bata abincinshi tana kai mashi amma Bashir yahana.
  Acikin yaranshi akwai babban yaronshi me suna Idi ana kiranshi da Jungle, shine yake bama Kawu shawarar yasa su sato mashi ita yabiya bukatarshi kawai. Kawu yayi murmushi yace kabari akwai tarkon danake dana ma Bashir saboda yanzu yaga yayi iyali shiyasa yamaidani abaya, duk wasu kadarorinshi yasaka sunan yarinyar nan ajiki, ka kyaleni dashi, yacemun zeje lagos, kuma nayi mashi magana akan inason wasu kudi masu yawa, inaso yabani su sannan in aikata mashi. Dariya suka sa gaba daya.

Zaune suke adaki Bashir yace Hajjo wlh kawu ya matsamun, gani yake kamar wasu kudade gareni, shiyasa yake tambayata kudi akai akai, mika mata wasu takaddu yayi da check na banki yace wannan takaddun gidan nan ne, wannan check din kuma na bankin Falak ne, domin aciki nake ajiye duka kuda dena,inaso kiyi masu boyo sosai, dan nayi alakawrin bazan kara bama kawu kudi masu yawa ba, koda yaje yaduba account dina baze samu komai ba, dan besan da wannan account din na Falak ba, tunjiya dana dawo daga Lagos yakeson ganina ni kuma boyewa nakeyi, se dazu yamun maganar kudi nace mashi banda kudi nayi asara sosai, yanzu mota ta ma zansa kasuwa insamu inbiya mutane kudinsu.
   Haka yatashi yatafi yana bambami, tashi Hajjo tayi taboye. Abinda yabata sannan tadawo kusa dashi tazauna tace Dadyn Falak hakuri zamuyi da halin kawu, ni kaina ina tsoron shi wlh, kana ganin irin yanda yake sakama Falak ido, banaso wata rana yayi mata.......... Bata karasa maganar datakeyi ba, sukaji an banko kofar dakin, wasu mutanene suka shigo , kuka Hajjo tafara tana fadin shikenan munshiga 3. Marin da,aka yimata ne yasata yin shiru, anan suka kama Bashir suka daureshi da Igiya, kukan Falak suka jiyo abakin kofa, dasuri tafada jikin ummanta tana kuka, abinda suka ganine yanasu mamaki, Kawu ne yashigo yana dariya.

     Bashir yace kawu me muka yimaka arayuwa? Duk irin yanda nake yimaka biyayya amma baka gani, dariya Kawu yayi yace dama ai nafada maka, sbd haka yanzu zankashe ka kuma inmaida matarka da yarka dadirona, dan kasan tunda ka aurota nakejin kishinta, amma ka tare komai, ahaka har ta haifi yarinya me kyau, wadda naji bazan iya hakura da ita ba. Kuka sosai Bashir yakeyi sbd abinda yaji Kawu yana fada, ahankali yace kawu dan girman Allah kayi hakuri, wlh kome kakeso zanbaka kada kayimun haka, Kawu yace aikin gama ya gama, Bashir, yanzu da dukiyarka da iyalanka duk sun zama mallakina.
   Zeyi magana kenan, Jungle yakwantar dashi, hanin yafiddo wuka yasa Hajjo da Falak suka matsa kusa,da kawu suka kama kafarshi suna kuka suna rokonshi, karar dasukaji ne yasasu juyawa. Kwance suka ga Bashir cikin jini Jungle yayi mashi yankan rago.
    Anan take Hajjo tafadi kasa asume. Kanta Falak tayi tana kuka,
   Anan kawu yasa su Jungle, suka dauki gawar Bashir yace suje can cikin daji su gina rami su rufeshi, bayaso subarshi batare da sunrufe shiba.

   Bayan awa 2 su Jungle suka dawo, afalo suka iske Hajjo da Falak adaure se kuka sukeyi, anan kawu yace masu suje su kwaso mashi kayanshi su dawo mashi dasu nan, yace kasan yanzu nine megida, anan zan zauna har Hajjo tagama iddarta sannan na aureta, ita kuma Falak sa daka zanyi da ita. Dariya suka sa gaba daya, Jungle yace Oga tunda kadauki uwar dani kabama diyar ai.

Hade fuska kawu yayi yace banaso kana kawomun wasa acikin iyalina. Dariya suka kara sawa. Kawu yace jungle gobe kaje gurin malamin can katambayomunshi Shekara nawa macen da mijinta ya mutu takeyi kafin takara wani auren.
     Dariya jungle yayi yace haba Oga ai sekasa ayi mana dariya kamata inje ina tambayar yanda ake idda, kasanfa nima nayi islamiya. Kawu yace yauwa, shikenan ma, fada mana muji, dan data gama zamuyi aure, kasan komai inaso inyishi yanda Allah yace kada inyi aure akan aure.
[7/6, 1:17 PM] YAYA HAYAT: ???????????? AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Part 15.....20

 Dariya sauran sukayi, kowa yana sauraron abinda Jungle zece, Hajjo ta kalli Falak wadda idanuwanta harsun kumbura saboda kuka, kai ta girgiza hawaye suna kara zubo mata a idonta, jin irin rashin mutuncin da Kawu kemasu.
    Jungle yace ai Oga bata wuce shekara 1. Murmushin jin dadi kawu yayi yace haka nakeson tafiya damasu ilimi, ina ganin idan zamuyi aure kaine waliyina.
     Kallon Hajjo kawu yayi yace daga ranar dakika gama iddarki aranar zaki zama matata, kuma inaso kije kidauko mun takaddun gidan nan, idan bahaka ba wlh agabanki zan keta mutuncin diyarki. Dasauri Hajjo tace wlh zan dauko maka akwanceni dan Allah kada kataba mun Falak. Kome zakamun inde bazaka taba Falak ba, nayarda. Sawa yayi aka kwanceta ta tashi tanufi dakin Bashir tana waigen Falak.

Check din daya bata tafitar tadauko wata karamar jaka wadda tasa awarwaron Falak aciki tasaka check din sannan tadaura ta akugunta tayi saurin fitowa, tana zuwa tabashi, amsa yayi yana murmushi, yace saura kudi, tace kawu kasan Bashir beda kudi, dazu yake cemun zesayar da motarshi ma, kawu yace anyi haka, Jungle daga yau munyi mota.

Tashi yayi yacema su jungle zaku iya komawa gidana nabaku, nikuma ina nan, ke Hajjo keda diyarki ku koma dakin ki dazama ni kuma zankoma dakin Bashir, Sawa yayi aka kwancesu, yace wlh duk ranar da kikayi kokarin guduwa sena kasheki diyarki kuma tazama tawa, ke babu ba hanyar tazaki fita sbd zansa tsaro me kyau. Garama kun kwantar da hankalinku munyi rayuwar jin dadi. Tashi yayi ya sallami yaranshi shi kuma yawuce dakinshi domin kusan karfe 3 saura. Haka su Hajjo suka koma dakinta suna kuka, Falak tace shikenan yanzu umma haka zamuyi ta zama kawu yaci bulus kenan? Hajjo tace inaso kada ki daga hankalinki muyi hakuri komai yayi farko zeyi karshe, insha Allahu bazamu dawwama ahaka ba. Tashi tayi ta dauko duk wasu takaddun Falak da zinaranta dana Falak taciro jakarta tasakasu ciki ta maidasu akugunta . Falak tace Umma meyasa kika dauresu anan? Tace insha Allahu zamu fita daga gidan nan, koni banfita ba, ke zaki fita, nasan wadan nan kayan zasuyi maki amfani. Falak tace Umma kidena fadar haka, idan har kina gidan nan to tare zamu zauna , tashi sukayi suka dauro alwala suka fara nafila.

Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya, kullum Hajjo ita da Falak zasuyima kattin Allah girki, Hajjo tahana Falak zuwa makaranta, sbd harin da yaran kawu suka taba kawo mata ranar data dawo islamiyya.
Kullum kawu cikin kirga watanni yake,  alokacin har Hajjo tagama iddarta besani ba, danshi kirgen shekara yakeyi, ita kuma taki tafada mashi, ko dan kunne daki sakawa dan bataso yagane ta. Kullum cikin tunanin hanyar dazasu gudu take, amma ina, kawu yasamasu matakan tsaro.
    Aranar da Bashir yacika wata 5 da mutuwa, aranar su kawu suka fita wani aiki da dare,suka bar mutum daya domin yayi gadinsu Hajjo, Jungle yace Oga kana ganin babu matsala abar mutum daya? Kawu yace ayanzu Hajjo ta hakura dazaman gidan nan, tasan idan ta tafima bata da gurin zuwa, kada kadamu muje kawai.

Bayan tafiyarsu da awa1 Hajjo taleka, murnace takamata ganin megadin yana bacci, komawa tayi tadauko wani karfe, tazo kusa dashi, tadaga karfen ta kwada mashi akai, nan take yayi kara yafadi asume, komawa tayi tacema Falak tadauko hijabinta takama mata hannunta suka fita suka fara gudu.
   
   Alokacin dasu kawu suka dawo asume suka samu megdin, cikin sauri yashiga vikin gidan, babu inda be duba ba, amma begansu ba, fusace yafito alokacin har megadi yasha ruwa ya farfado, shakoshi kawu yayi yace suna ina? Megadi yana zare ido yace wlh nima ina. Kwance naji saukar wani karfe bankara sanin inda kaina yake ba, se yanzu. Kawu yace kufita nasan duk inda suke basuyi nisa ba, ku kamomunsu.


Gaji labarina Alhaji, kuma ina me tabbatar maka babu karya ko daya acikin labarin dana baka, idan har karya nake maka kada Allah yamun......saurin rufe. Mata baki yayi, yana me girgiza mata kai, shikanshi wahaye ne suke fita acikin idonshi.
      Hannunshi yacire yace wlh Hajjo nayarda dake dari bisa dari, bakiyi kama da marar gaskiya ba. Hakika labarinki abune me girgizawa, dole duk wani me imani ya tausaya maku, lallai kunga rayuwa wadda ba duka mutum bane ze iya daukar kaddarar da Allah yadora maku.
     Nayi alakwarin rikeku bisa gaskiya da amana. Hajjo inason infada maki wata magana sede ina tsoron kimun wata fassara, ko kuma kice sbd na temakeku ne yasa zance haka. Hajjo ta goge idonta tace wlh babu abinda zaka nema agurina bnyi maka shiba, kafadi abinda ke ranka.
   Shiru yayi sannan yadago kai yana kallonta yace Hajjo bazan iya boye maki ba, agaskiya tun bayan mushigo gidan nan nadora idona akanki Allah yasakamun sonki araina. Idan harzaki amince dani ashirye nake dana aureki kuma inrike Falak tamkar diyata. Matata daya Zarah da yarana 2 mata, Jidda da Jalila, inaganin Jalila zasuzo sa,anni da Falak.

Murmushi takeyi kanta akasa haryagama bayaninshi. Yace Hajjo kinyi shiru bakice komai ba, kada kidamu idan har bakida ra,ayin aure yanzu na amince zan zamo yayanki kuma mahaifin Falak wlh babu damuwa. Kai tadago tace bakomai Alhaji inaso kabari zuwa gobe zanyi shawara da Falak. Murmushi yayi yace badamuwa Allah yakaimu goben, kije ki kwanta dare yayi natsareki nikam yau babu barci, tace sbd mene? Yace yau kam ai buzu zan hau naneman sa,ar gobe. Dariya tayi tashige daki. Murmushi yayi yakwanta bisa kujera, hakanan yakejin wani farin ciki yana shigarshi , godiya kawai yakema Allah daya bashi ikon temakonsu Hajjo.

Washe gari dasafe bayan sunyi sallah sukayi wanka, anan Hajjo takalli Falak tafadi mata duk yanda sukayi da Alhajin daya temakesu, Murmushi Falak tayi tace wlh Umma ki amince mashi, kinga zamuyi nesa dasu kawu, bazasu taba tsammanin muna kaduna ba, kinga hankalinmu ze kwanta sosai. Hajjo tace Falak amma fa yana da mata hada yara 2, ina tsoron tashin hankali. Falak tace  Umma kowafa da halinshi ze zauna, mude muyi kokarin zama da duk wanda Allah yahadamu zama dashi tsakanin mu da Allah. Hajjo tace hakane, Allah yazaba mana abunda yafi zama alkhairi.
    Fita sukayi afalo suka sami Alh. Har yadawo daga cikin gari yakawo masu abin karyawa. Bayan sungaisa Alh, yamika masu abincinsu shima yaja nashi suka faraci. Falak tafara tashi takoma daki, kamar jira yakeyi yasauko kasa yace Hajjo wlh banyi bacci ba jiya amsarki kawai nake jira. Fuskarta ta rufe da hijabinta tana murmushi, yace kin amince? Kai tadaga mashi, godiya sosai yayi mata, yace sufito sukama hanya.

Zarah ce take tafaman gyara gida sbd megidanta zedawo, Jalila da me aikinsu Mairo suna kitchen suna hadamasu abinci. Jidda kuma tana dakinsu tana wanke bandakunan gida. Misalin karfe 2 na rana kowa yashirya suna jiran zuwan Alhaji. Jidda tace wlh nakosa Dady yadawo nasan zemana tsaraba sosai. Zarah tayi murmushi tace ai kunsan kowace tafiya idan Alhaji yayi tsarabata tafi takowa girma. Jalila tace kai Umma yaude tamu setafi taki tsoka, dariya suka dukansu, anan sukaji karar bude gate, da gudu suka fita domin taroshi, Zarah tashige daki domin kara gyarawa.

Mamakine yakamasu ganin Dadynsu dawasu mata, hakade suka yimashi sannu dazuwa suna kallonsu Falak, Jidda aranta tace kai ammade wadannan sunada kyau, tsayawa sukayi domin karbo tsaraba. Se sannan Alh. Yatuna bema yimasu tsaraba ba sbd tsabar farincikin amincewar Hajjo. Alh, yace mushiga cike yau babu tsarabar ci sede ta mutane, ciki suka wuce kowa da irin abinda yake rayawa aranshi.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(  Nabeelert Lady)
08028525263
[7/7, 9:54 AM]  ???????????? AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Part 20.....25

Da sallama suka shiga cikin gidan, cike dasauri Zarah tafito tayi kyau se kamshi takeyi zuwa tayi ta rungume megidanta tana dariya, shima dariyar yakeyi.
   Janshi tayi zuwa daki, su Hajjo suna tsaye bakin kofa, Jalila ce tajasu zuwa wani daki, bandaki ta nuna masu sannan tashimfida masu abun sallah tafita domin kawo masu abinci da ruwa, bayan sunyi sallah sukaci abincin da Jalila takawo masu.

Atare suka fito bayan yayi wanka, yafito cin abinci, zuba mashi tafarayi, saurin tashi yayi yana kiran Jidda da Jalila, bayan sunzo yace ina bakin da mukazo tare? Jalila tace suna dakin baki sunyi sallah suna cin abinci, ajiyar zuciya yayi yace yau Jalila nagode.
    Ya mutsa fuska Zarah tayi tace Alh, wane irin baki ne suka shigomun gida bansan da zuwansu ba, zama yayi yafara cin abincin shi yana murmushi. Zamatayi kamar zatayi kuka tace ina magana amma kayi shiru, haba hajiya, ai komenene kinbari ingama cin abinci ko.

Zaune suke afalo suduka, ayayin da su Hajjo suke zaune kasa. Zarah se cika take tana batsewa, Hajjo duk jikinta yafara sanyi ganin irin kallon da Zarah take yimasu, ko gaisuwarsu da kyar ta amsa, dama Zarah batason mutane, bare kuma dataga kyawawan mutane suzo tare da mijinta.

Gyaran murya Alh, yayi anan yayi masu bayani akan su Hajjo, har labarinsu seda yabasu. Jalila se kuka takeyi, gaba daya tausayinsu yakamata. Jidda da Zarah kuwa yatsuna fuska sukayi, zuciyar Zarah kamar zata fashe dan haushi.

Alh, yace sbd haka nakawosu gidan nan inafatan kuma zaku rikesu tamkar yan uwanku.... Zarah tace dan Allah Alh, dakata, kayi mani bayani yanda zanfahimta, idan ma masu aiki ne ka kawomun ni banida bukatarsu, inada me aiki, dan gaskiya wadan nan sadakar yallan bazasu zauna mun agida ba, idan ma temakonsu zakayi kabasu kudi sukama gabansu.

Murmushi Alh, yayi yace Zarah ai baki tsaya kika gama jin abinda zance ba ko, kinrufeni da fada kamar kinsami wata Jidda ko Jalila, kuma dan rashin mutunci agaban mutane zaki rufe ido kina fadamun abinda kikaga dama.
   Ina fatan acikin bayani na danayi bakiji nace zan ajesu agidanki ba. Agidana nace zan ajesu ko? Dan haka ki kula da kalamanki. Kuma wannan dakike gani Hajjo, insha Allahu cikin satin nan za,a daura mana aure, Falak kuma zanriketa kamar yanda zanrike Jalila ko Jidda.
    Bana son inkara jin wata magana kuma Jidda ku kiyaye, dan haka wancen part din acan zasu zauna, bance ku hada girki ba, kowa nashi zeyi, abinda nakeso asamu zaman lafiya acikin gidana, kinfi kowa sanin halina banason tashin hankali ahakan yasa bamu taba samun sabani nida ke ba, seyanzu. Dan haka ki kiyaye.

Jalila ga key din wancan part din nan zanyi magana da megadi kuje keda Mairo ku tsaya ya gyara idan nafita zansa akawo kaya azuba aciki dan yau nakeso su koma.

Murmushi tayi tace angama Dady, tashi yayi yace Hajjo kutaso muje. Fita sukayi suka shiga mota. Kasuwa yanufa dasu.

   Wasu irin zafafan hawaye ne suke zarya afuskar Zarah, tunda take da Alh, betaba yimata koda tsawa bace bare fada. Amma yau gashi sbd wasu banzaye yana fadi mata maganganu. Jidda tamatso kusa da ita tace haba Ummi meyasa sbd wannan maganar zaki daga hankalinki, tunda nataso agidan nan bantaba ganin kukanki ba seyau, tayama za,ayi inso wadan nan mutanen masu kama da aljanu.
   Wlh Ummi kinfi karfin yin kishi da fillo, ki kyalesu zaman gidan nan seya gagaresu, naso ace acikin part dimmu zasu zauna wlh damun samu. Masu aiki, amma bakomai idan sunsan wata basusan wata ba.

Jalila tace haba Yaya Jidda, da bakinki kike fadin wannan maganar, kada kimanta fa suma mutane ne kamar kowa, kuma ko ba komai duk abinda Dady yakawo gidan nan ai yakamata mudaukeshi da daraja, kuma ai...... saukar marin dataji ne yahanata karasa maganar datakeyi.
     Zarah tace dama batun yauba nasan bakida kishi akaina, nadauka kune masu goyamun baya aduk halin danake ciki, amma segashi dabakinki kike fadin wannan maganar. Wlh idan kinaso mushirya kifita aharkar wadannan mutanen, idan bahaka ba, kuma zamusa kafar wando daya dake. Tashi tayi tashige daki taci gaba da kuka, aduniya babu abinda ta tsana kamar kishiya, seyanzu take ganin wautar ta narashin mallake Alh, tuntuni ta biyema shawarar Karima, gashi nan duk irin kissar datakeyi mashi be hanata yimata kishiya ba. Lallai wannan tafiya ni akaimawa, kuma nasamu tsaraba me tsoka. Amma wlh duk yanda zanyi matar nan bazata dade agidana ba.

Kafin sudawo har angama gyaran part dinsu, masu kaya sunkawo ansaka aciki, komai yayi dede tun daga labule , kujeru, gadaje da kayan kitchen babu abinda ba,a saba, dakin Falak kadai ya isa ya burgeku, komai na bukata seda aka saka aciki sannan driver yashigo da kayan abinci yasaka a store ya kulle gidan, yatafi.

Se yamma suka gama siyayya lefe sosai yahada mata. Itama Falak babu abinda be saya mata ba, Hajjo har kuka tayi sbd murna, gidan abokinshi yawuce dasu, anan yayi mashi bayanin komai, matarshi Zainab mace me kirki ta tausaya masu sosai. Alh, yace inaso kuje muje gurin telanki domin abashi dinku nansu dan dawuri nakesonsu.
   
Farouk yace bakomai Dauko hijabinki muje nima inyi rakiya, abokina kace nanda kwana 5 zaka angwance, lallai wannan tafiya tayi riba.
     Seda ya gwadasu sannan Alh, yabashi kudin dinkinshi yace nan da kwana 2 azo akarbi kala 5 na amarya kala 3 na Falak zeyi kokarin kara wasu kafin biki, idan yaso sauran zuwa bayan biki se azo akarba. Godiya sosai, suka yimashi suka tafi. Basune suka koma gida ba se karfe 7 na dare, makulli ya amsa gurin driver suka nufi part dinsu yabude.
   
Mamaki ne yakama su ganin irin kayan da aka zuba agidan, duk da ba baki bane aganin irin kayan amma sunji dadi sosai. Bayan sunzauna. Hajjo tace Alh, bansan dawane irin. Baki zanmaka godiya ba, kagama mana komai arayuwa sede inroki Allah yabamu ikon saka maka da mafificin alkhairin daka yimana.

Murmushi yayi yace Hajjo basekin godemun ba, domin kingama mun komai tunda kika amsa zaki aureni, nima Allah yabani ikon kamanta gaskiya atsakaninku. Abinda nakeso dake ki kasance me hakuri, banason tashin hankali, kuma nasan baki dashi, kiyi hakuri da duk abinda zaki gani, daga gurin Zarah, nasani sarai bata da son mutane, shiyasa ma na ajeku anan, koda banida wannan part din bazan iya hadaku agida daya ba, dan haka kuyi hakuri dasu.
    Kuma insha Allah bayan biki Falak zaki cigaba dazuwa makarantar su Jalila. Nasan aji daya za,a saka ku tunda kince a ss 2 take , itama Jalila haka. Kome kukeso akwaishi akitchen, Falak inaso kidaukeni kamar mahaifinki, kada kiboyemun damuwarki dan Allah, kuma kizauna da yarana kamar yan uwanki. Godiya suka kara mashi sannan yayi masu seda safe yace su kulle kofar,

Adaki yasamu Zarah kwance, kusa da ita yaje yajawota yana fadin haba my luv yau kuma ni ake sharewa haka. Kinsan fa bamuyin haka dake, dan Allah kada kibari shedan yashiga zuciyarki yabata mana zaman lafiyar damukeyi na tsawon shekaru da dama.
    Murmushi tayi data tuna shawarar da Karima tabata, dazu fasuka gama waya, tace Zarah maza yan lallashine, idan harkinaso kimallake zuciyar namiji kozakiyi mashi asiri dole sekin hada da biyayya da kuma kissa, idan bahaka ba, kina zaune wata zatazo ta kwace maki miji, kawai ki kwantar da hnklinki ayi biki agama idan yaso da kssa ki koreta, amma idan kina tada hankalinki kome yafaru da ita ke za,a ce.

Kara rungumeshi tayi tasaka kukan kissa, tana fadin dan Allah Alh, kayi hakuri nayi nadamar yimaka abunda bantaba yimaka arayuwata ba se yau, kuma agaban ,ya,yanka da bakinka. Allah yasa haka yazama alkhairi, nide fatana kayi adalci atsakaninmu.

Sosai yaji dadin abinda tafada, dama yasan kishine yasata fadin abinda tfada dazu, goge mata hawayen idonta yayi yace nagode sosai matata, Allah yabiyaki, insha Allahu zaki sameni mecika alkawari, bazan taba juya maki baya ba, kema kinsan aduk duniya kece mace ta farko dana fara so, kece uwar yara na, babu abinda ze rabamu. Tashi sukayi tarakashi zuwa bandaki yyi wanka sannan suka kwanta.

Washe gari bayan yashiga sun gaisa dasu Hajjo yanufi gidan kawunshi, anan yafada mashi abinda ke tafe dashi, sosai kawunshi yaji dadin maganarshi, dan suma sungaji da halin matarshi narashin son mutane, yace bakomai Allah yakaimu asabar din, amma waye ze zama waliyinta? Yace abokina Farouk shine yace ze zama waliyinta. Yace to Allah yakaimu, kuma sekayi kokarin rike amanar marayun Allah daka dauko, yace insha Allahu kawu, anan yayi mashi godiya yatafi.

Ana saura kwana 2 biki komai ya kan kama har dinkunansu ankawo saura wadanda ba,a dinka ba, sosai sukayi kyau acikin kwanakin dasukayi, bakamar Falak, kyawunta yakara fitowa, Jalila kadai take shigowa part dinsu dan ita hakanan takeson Falak, amma Jidda da Zarah tunda sukazo basu kara sakasu aido ba, dan Hajjo macece wadda batason wulakanci shiyasa ta tsorata da irin abinda Zarah tayi masu, hakan yasa bata kara shiga part dinsu ba. Duk yanda Alh, yaso tashiga amma tace itade tsoro takeji yabari bayan biki tashiga.

Sallama aketa kwadawa acikin falon, da kyar Zarah tafito tana yatsina ta amsa sallamar. Ahankali tace tofa yau kuma Inna Asabe ce agidanmu, washe baki tayi tace wlh Babanki ne yace kwana 2 bakizo ba, shine yace inzo inga ko lfy. Zama tayi tace tokema Inna banda abunki tunda kukaji shiru ai kunsan lafiya ko, amma kinwani kwaso kafa kintaho.

Ran Inna yabaci dajin maganar Zarah, amma dayake ita Allah yayita da shegen kwadayi yasa tace ayi hakuri hajiya. Anan tasa Mairo takawo mata abinci da lemu, zama tayi tanata zubi tana zuba surutu.

Zarah tace Inna namanta banfada maku ba, Alh, aure zeyi fa. Cike da mamaki tace haba Hajiya wace irin magana kike fadi haka, kamarki ace wai za,ayi maki kishiya kuma kizauna kina fada ma mutane, aini atunanina mutanen kauye wadanda basu waye ba, sune akema kishiya, yanzu duk cikin kawayenki wakika gani da kishiya? Gaskiya bazata sabuba ayima yata haka.
   Matsowa Zarah tayi jin irin maganar da Inna take fada. Asabe tace wlh na dauka tuni kingama da Alh, seyanda kikace yakeyi shiyasa bandamu davkawo maki maganin mallaka ba, kina tunanin duk son dayake maki idan matarshi tafara haifa mashi namiji agida baze manta dake ba. Gaskiya bazata yuwu ba.

Zarah tace yauwa Innata dan Allah kifadamun abinda yakamata inyi, dama neman abunyi nake, segashi Allah yakawoki, wlh konawa zan iya kashewa inde za,a fitarmun da wannan fulanin agida na. Murmushi Asabe tayi aranta tace anzo gurin, tunda baki badawa dan Allah yanzu kam lokacina yayi nima dazanyi arziki, wlh sena ta tseki kamar me.

Asabe tace kada kidamu acan zariya kinsan munada manyan bokaye, dan haka akwai kawata Dije tana da wani hamshakin boka, inaso bayan biki kizo muje gurinshi kome kikeso za,ayi maki. Godiya sosai Zarah tayima Asabe harta manta da irin abunda takeyimata dazu, Zarah tace yauwa Innata ainasan koda nayi rashin Uwa bazanyi kuka ba tunda ina dake, amma de anan zaki kwana zuwa gobe se insa driver yamaida ke ko. Mamaki sosai Asabe tayi jin yau tasamu matsayin kwana agidan Zarah. Anan suka cigaba da firarsu

Urs
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525
: ???????????? AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ (H,O,N,A)

Part 25.....30

Ayau asabar aka daura auren Alhaji Abba da Hajara akan sadaki naira dubu 30, mutane dayawa sunsami halartar daurin aure.

   Acikin gida kuwa babu wanda yazo ta bangaren Zarah daga Karima se Inna Asabe, dan yanzu sosai Zarah take mutunta ta, sbd zata kawo mata mafita amatsalarta. Tare da kawarta tazo wato Dije, sunci sun sha sunkuma kwashi ganima.

Jidda kuwa alokacin bikin ma bata kwana gida ba, tana can gidan kawarta Ameera bayan sundawo daga party suka wuce gidansu Ameera acan suka kwana.
   Jalila ce itada mairo me aikinsu suka shiga bangaren su Falak suka tayasu aiki, matar farouk ma tazo, sekuma yan uwan Alhaji.
   Hajjo tayi kyau sosai, idan kaganta bazaka ce Hajjo daga sani bace a wata 5 dasuka wuce, ita kanta tasan rabonta da farinciki irin na yau tunkafin mutuwar mijinta.

Haka akayi biki kowa ya watse aka bar amarya da diyarta agida, Jalila ce ita da Falak zaune adain Falak. Jalila tace wlh Falak nakosa asakaki makaranta nima insamu abokiyar tafiya, musammamma islamiyya, banida kawar tafiya, dan Yaya Jidda tadena zuwa kuma Ummi tahanani infadama Dady. Falak tace ai gara kada kifada mashi, addu,a kawai zaki tayata, kinsan kowa da irin tashi kaddarar. Jalila tace haba Falak, ko kinsan jiya ba,a gida yaya ta kwana ba, wlh ina matukar jin bakincikin halin da yaya tasa kanta, wlh ko sallah ba sosai takeyi ba, idan namata magana karshe zagine zebiyo baya.
    Falak tace tabbas Yaya Jidda tana cikin jarabawar ubangiji, sede muyi ta mata addu,a Allah yashiryeta, kuma kada kibari Dady yafara jin maganarta abakinki tunda kinsan abinda Ummi tace. Jalila tace nagode Falak bara intafi kada Ummi tanemeni.

Zaune suke gaba dayansu a falon Alhaji, Zarah tana zaune akusa dashi, bakaramin dauriya tayi ba, wajen boye damuwar dake zuciyarta. Hajjo ko gaba daya tsoro yahanata sakewa ta kosa takoma part dinta.
   Alhaji yayi gyaran murya yace, Alhamdulillahi, Allah yanuna mana wannan rana damuke fatan zuwanta.
Zarah takanki zanfara, kece Babba, inaso dan Allah, kamar yanda nasanki bakida fitina acikin gidan nan, haka nakeso kicigaba dazama ayanda nasanki, ku hada kanku, kidauki Hajjo tamkar kanwarki, kuma kirike Falak tamkar Jidda ko Jalila, abanson kubari wasu suzo susamu damar tarwatsa farin cikin damuka gina shekara da shekaru acikin gidan nan. Allah yabaki hakuri akan wanda kikeyi, banyi auren nan dan bana sonki ba, ko kuma da niyar in wulakanta kiba,nayi ne domin ina bukatar hakan, kuma dan inraya sunnar Manzon mu.

Kema Hajjo, inaso ki saki jikinki acikin gidan nan, kidauki Zarah kamar yar uwarki, da yayanta amatsayin naki, banason wata fitina, duk abunda baki ganeba nacikin gidan nan zaki iya samun Zarah ki tambayeta, ko kuma ni kitambayeni.
    Maganar girki kuma dama nafada maku, kowa nata zata rikayi, Hajjo idan kina bukatar me aiki Zarah kisa Mairo tasamo mata, ko kuma idan zata iya tarika yimaku ku biyu, ko ya kikace Hajjo? A,a bakomai Alhaji, ai aikin ma bawani meyawa bane, zan iya yi nidaya, tacigaba dayima Umminsu Jalila, idan ina bukatar wani abu zansa mairo tayimun.

Zarah tace haba Alhaji ai base anakara kawo wata me aiki ba, Mairo ma ta ishemu, Fatana Allah yabamu zaman lafiya, kuma Hajjo dan Allah kiyi hakuri da abinda nayi maku farkon zuwanku, sharrin shedan ne. Hajjo tace lah, ai babu komai.
    Muemushin jindadi Alhaji yayi yace, to Zarah yakike ganin za,a yi gurin raba girki? Zarah tace bayan kagama kwana 3 ina ganin muyi kwana 2 ko hajjo? E duk yanda kikace yayi hakan. Alhji yace to Allah yabani ikon kwatanta adalci atsakaninku. Bara muje mukwanta naga dare yayi, tashi Hajjo tayi tamata seda safe tawuce, jawo Zarah yayi ya rungume, kwallar data ke boyewa ce tazubo, saurin kifa kanta tayi bisa kirjinshi. Kara rungumeta yayi yana lallashinta, da kyar yasamu tabarshi yatafi.


Haka rayuwa tacigaba datafiya cike da kwanciyar hankali, ansaka Falak makarantar su Jalila,inda aka sata a ajinsu Jalila SS 2, alokacin su Jidda suna shirin gamawa, sosai take gane karatun, dama Falak bade kokari ba, cikin lokaci kadan tazama zakaran ajin, hatta da malamai sun santa. Babu abinda ke hadata da Jidda, dan bakaramin Tsanarta Jidda tayi ba, sbd kyan datake dashi, ko magana tayi mata bata amsawa, amakaranta idan akaje daukarsu tarinka fadama kawayenta ga AGOLAR gidansu nan, abun yana matukar damun Falak, kullum sede Jalila tarika bata hakuri, duk irin cin mutuncin da Jidda takeyi mata bata taba fadama Ummanta ba, sbd tasan Ummanta dasaurin damuwa.

Zaman gidansu Zarah zamane na kissa, domin baka taba gane Zarah batason Hajjo, duk da bawani shiga part din juna suke sosai ba, amma tana nuna mata so.kuma Alh, yana iya kokarinshi akansu, babu abinda suka nema suka rasa, duk irin kudin da yake basu Hajjo bata siyan komai, sbd acewarta babu abinda suke bukata. Hakan yasa taroki Alh, dasuje ta duba account din Falak, tanaso ayi mata ATM, sannan tacigaba da ajiyar kudi aciki.
     Tare sukaje akayi mata komai, sannan tasaka dukan kudin datasamu abiki da kuma wanda yake basu,


Bayan wata daya da bikinsu, Hajjo tafara laulayi, zazzabi me zafi takeyi, hakan yasa Alh, yaduketa suka tafi asibiti, suna zuwa awon farko akace tana da shigar ciki na sati 3. Murna agurin Alh, kamar ba,a taba yimashi haihuwa ba, bayan sundawo gida yawuce part din Zarah. Anan yake fada mata cikin Hajjo, Da kyar Zarah ta dedeta kanta sbd wata irin faduwar gaba ce tazo mata jin Hajjo tana da ciki, murmushi tayi tace kai amma naji dadi, ai gara mukara samun yara agidan, amma wadan nan ,yan matan dasunyi aure shikenan gidan ze koma shiru. Alh, yace wlh kuwa, Allah de yasa tahaifa mana aboki. Dif murmushin fuskarta yadauke, shi bema kula da yanayin data shiga ba, haka yayi ta zuba, daga karshe yakoma part din Hajjo.

Wata irin zufa taketo mata, daki tashiga, tarasa abunyi kawai tasaka kuka. Lallai namiji ba abin riko bane, wai yau Alh, dakanshi yake maganar ahaifa mashi yaro, wato sbd yaga niban haifa mashi ba. Wlh dole gobe inje Zariya, nadena kaima Karima kuka na, dan naga idan nabiye mata zata kaini tabaroni, yanzu lokacin kissa da biyayya sunkare dole se boka yashigo cikin al,amarin nan. Allah yakaimu gobe da safe.

Washe gari dasafe ko abinci Zarah kasa ci tayi, haka su Jalila suka gama shiri sukayi mata sallama, tace masu zataje zariya kilama ta kwana. Sukansu sunyi mamakin jin kalmar zuwa zariya abakin umminsu, kuma ma har maganar kwana takeyi, ganin kamar suna yimata wani kallo yasa tace masu Inna ce bata da lafiya. Sukace Allah yabata lafiya, idan kinje kiduba ta.

Segurin karfe 9 Alh, yashigo, alokacin Zarah harta shirya jiranshi kawai takeyi, sanin Alh, bame hana zuwa unguwa bane shiyasa bata damu da seyanzu zata fada mashi ba.

Bayan sungaisa yace waini Zarah ina zuwa naga kinfito da jaka da gyale? Murmushi tayi tace wlh jiya bayan kafita akamun waya daga gida cewar Inna batada lafiya, to ganin dare yayi shiyasa banfada maka yau zanje ba.

Ashsha, meyasa meta? Tace gsky basu fadamun abinda kedamunta ba, amma idan naje zanji,sede gobe nakeso nadawo. Mamaki ne yakama Alh, sede yaboyeshi dan bakaramin dadi yaji ba, dayaji Zata kwana agidansu, acewarshi kila tafara canza halinta ne. Shikenan babu damuwa Allah yakiyaye hanya, kinga akwai inda zanje aida muntafi tare, amma idan nasamu lokaci zanje indubota. Zarah tace ai bakomai idan najema yawadatar, zanhadaku awaya. Yajikin Hajjon? Murmushi yayi yace jikinta dasauki ai tasha magunguna. Daki yashiga yadauko mata kudin naira dubu 100 yace tarikesu ahannunta ko za,anemi wani abu, godiya tayi mashi, yawuce yafita, tace gata nan zuwa ta duba Hajjo. Mairo ta kwala ma kira kasancewar anan take kwana, dan dattijuwa ce. Bayan tazo tafada mata zataje gida se gobe zata dawo. Ita kanta mairo tayi mamaki, duk abinda zasu bukata ta bata sannan tawuce part din Hajjo.

Bayan ta dubata ta tashi zata tafi, Hajjo tashiga daki tadebo sabulan wanka dana wanki masu yawa tace akaima Inna, godiya Zarah tayi mata sannan tafita aranta tana fadin abanza wlh, babu abinda zesa naji tausayinki, haka nan daga zuwanki keda waccan shegiyar AGOLAR taki kunaso ku mallakemun miji.

Murna duk tacika Inna da Baban Zarah ganin yau Zarah ce agidansu kuma harma zata kwana, Inna tace Malan ai yakamata ka koma kasuwa hakanan kazo ka tsaya acikinmu kamar mace, jiki na rawa yace wai da zama zanyi mugaisa da Zarah ta, tunda taxo ai yau babu batun kasuwa kuma. Zarah tace Baba kaje kawai ai anan zan kwana yanzu akwai inda zanje. Inna tace idamma kazauna mezaka bata, yace shikenan to sekun dawo, haka yafita Inna tana binshi da harara aboye, abinda baku sani ba, Asabe tadade da mallake Baban Zarah, dama kuma tahanyar asiri tashigo gidan, dan Asabe muguwar yar tasha ce dan ba,a cikin Zariya take ba,yawon iskancinta ne yakawoya zariya harta hadu da Baban Zarah, Kawarta Dije ta tsaya mata har ta aureshi, kuma tayi sanadiyar mutuwar uwar Zarah ta mallakeshi take zaune agidan, ko Zarah tarasa yanda zatayi da ita ne shiyasa take zaune da ita, dayake ta iya kissa, hakan yasa mutanen gari suke ganinta kamar ta kirki. Ganin Zarah ta auri me kudi yasa ta saduda tamaida kanta sakarai agurinta saboda itama tayagi rabonta
Se gashi Allah yakawo mata hanyar sauki dazata ci kudinta aruwan sanyi.
   Bayan Zarah tabata sabulan da Hajjo tabada akawo mata, Asabe tace kinga irin kissar tata ko, ina nan dake idan alh, yazo seta fada mashi abinda tabada aka kawomun,tashi muje gidan Dije, wannan bazesa mukyaleta ba. Alh, baze kara haihuwa da kowa ba, sede ke. Murmushin jindadi Zarah tayi tace shiyasa nake sonki Innata, yauwa ga waya ma nataho maki da ita, nasaka maki layi aciki sbd idan inason wani abu basena nataso nazo ba, banason Alh, yafara zargin wani abu, tunda yasan bazuwa nakeyi sosai ba. Asabe tace dama Hajiya tunda kinada mu agari ai kinwuce kije gurin boka da kanki, aisede kibamu umarni muyi, godiya tayi mata, sannan suka nufi gidan Dije, daga can suka wuce gurin boka, dama Dije ba miji gareta ba.

Abakin bukkar bokan Dije tace sujirata tashiga akwai maganar dazasuyi dashi, kashe ma Asabe ido tayi sannan tashiga, dayake boka natane, anan tayi mashi bayanin abinda takeso yacaji Zarah, dakuma kasanshi idan tabayar, da abinda zasu dauka ita da Asabe.

Fita tayi suka shigo tare. Bayan Zarah tagama yimashi bayani, Boka yayi dariya yace cikin kikeso alalata ko kuma akasheta gaba daya? Fiddo ido tayi, tace boka bazan iya kashe mutum ba, kawai a lalata cikin, idan yaso daga baya da kaina, nasan yanda zanyi inkoreta. Boka yace aikinki yana da tsada, amma sbd wadan nan zanyi maki sauki. Zarah tace boka kudi badamuwata bane, konawa zanbiya inde za,a cire cikin. Boka yace kije can kidaga wancan kwaryar kisaka dubu 150. Tashi tayi jiki na rawa taciro kudin tasaka. Wata diyar roba yadauko hannunshi yasa abisa cikinta yarika wasu surutai, yana murza cikin, wata kara sukaji anyi, Zarah takama Asabe tarike, aje diyar robar yayi yace matso nan ki gani, wata kwarya me ruwa aciki yadauko nan take hoton Hajjo yafito, tana kwance se juyi takeyi akasa, kafafunta kuma jini yana fita. Boka yace cikinne yake fita, angama da wannan matsalar, se nakara ganinki. Tashi sukayi suna mashi godiya.zasu fita boka yace Dije ke kitsaya.
   Bayan sunfita, boka yace gaky Dije kun kawomun matar dazan ci kudi kuma kuci, lallai bayanzu zan sallami wannan matar ba, semunci kudinta, sosai, kudin yadauko yadauki dubu yadauki dubu 80 yabasu 70, godiya Dije tayi mashi tace semun sake dawowa.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263

[7/8, 4:02 PM] YAYA HAYAT: ???????????? AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)

@( H,O,N,A)

Part 30..... 35

Falak ce tayi sallama tadawo daga makaranta, kaitsaye dakin Ummanta tanufa, cikin sauri ta ajiye jakarta takarasa gurin Ummanta, ganinta kwance cikin jini tana nishi.
   Kiran sunanta tafarayi tana kuka, ganin takasa amsa mata tayi waje da gudu domin kiran driver, fitar ta yayi dede dashigowar Alh, tsaya wa tayi haryayi parking, dasauri ta isa gurinshi, tana kuka.
   Fitowa yayi yana tambayarta lfy? Tace Umma ce batada lafiya. Ai bejira ta idasa ba, yayi hanyar part dinsu. Yana zuwa yaga halin datake ciki , hijabinta yasa mata yadauketa, Falak tana biye dasu, mota yasata, Falak na kokarin shiga sega Jalila. Alh, yace yauwa Jalila zamuje asibiti Hajjo ba lfy, ku kula da gidan. Shiga yayi yaja suka tafi.

Suna zuwa aka wuce emergency da ita, Alh, se zagaye zagaye yakeyi, Falak ko se kuka takeyi, shikan shi Alh, tabashi tausayi. Seda suka dauki minti 30 sannan aka fito da ita abisa gado aka nufi, dakin da aka bata da ita, bin bayanta Falak tayi, shikuma yabi bayan likitan.

Zaune suke a office, Dr, yace Alh, sede kayi hkr cikin dake jikinta yazube. Sede bamu samu wani dalilin daze nuna mana abinda yayi sanadiyar zubar cikin ba. Amma alhamdulillahi, babu wata matsala atare da ita, anyi mata wankin mahaifa, kuma anyi mata allurai, insha Allahu zuwa dare ma zaku iya tafiya, semunce Allah yakawo wani me amfani. Zufar data fitoma Alh, agoshi yagoge, sannan yace ameen, Dr, nagode. Sosai yaji ciwon zubewar cikin sede babu yanda zeyi dole yayi hkr da hukuncin Allah, tashi yayi yanufi dakin da suke.

Zauns suke adakin Asabe, Zarah tace gaskiya Inna nagode maki, yanzu nakara tabbatarwa banida sama dake, dana tsaya bin shawarar Karima dayanzu ina can ina tagumi. Kome kenan idan akwai wata matsala, zanyi maki waya sekuje gurin bokan, basena zoba, idan kuma takama dole senazo se inzo din.
Wayarta ce tayi kara, ganin Alh, ne yake kira yasata saurin dagawa, jin muryarshi cikin sanyi, yasa tace lfy de Alh, naji kamar wani abu yana damunka, naji muryar kasa kasa.
   Anan yafada mata abinda yafaru, salati tafarayi cike da damuwa kamar zatayi kuka tace Alh, gani nan tahowa, tunda ko la,asar ba,ayi ba. Yace aa kibari se gobe, tunda itama Inna bata da lafiya. Tace a,a ai taji sauki, nide bazan iya zama ba, Hajjo tana da bukatata akusa yanzu, kasan su Falak yara ne, dole asamu wata babba akusa da ita, tunda Mairo aiki yayi mata yawa . Sosai yaji dadin yanda Zarah ta nuna kulawarta akan Hajjo.
    Bayan sunyi sallama tayi murmushi tace lallai aikin boka na kyau, Asabe tace meyafaru? Dije tace ai base an fada maki ba, kema kinsan cikin yabi ruwa. Dariya suka sa suduka. Zarah tace dani kike magana Hajjo. Bara intashi intafi, kada yamma tayi. Kudi tafiddo dubu 2000 tamika masu tace ga wannan asayi magi, godiya sukayi mata, suka rakata har mota, tazo shiga kenan Babanta yadawo, yace a,a Zarah ina kuma zaki? Tace wlh yanzu Alh, yamun waya abokiyar zamana tana asibiti, shine nace gara intafi. Baba yace wayyo Allah yabata lafiya, amma kin kyauta. Allah ya kiyaye hanya kidubata idan kinje. Dubu 1 tamika mashi tace Baba ga wannan anyi cefane, godiya yayi mata yanata shimata albarka, har ta tafi. Asabe tace malam kawo indauki kudina najiya, kasande ai baka baniba ko? Kamar zeyi kuka yace haba Asabe wlh koda naje kasuwa babu abinda nasamo, kuma idan nabaki dari 500 dama kuma meshago yana bina dari 300, kinga kudin sunkare, dan Allah kiyi hkr zanbaki. Dije tace a haba malam kabarshi wasa take maka bakomai tabar maka. Godiya yashiga yimata, anan yawuce masallaci, sukuma suka nufi gida.

Dije tace wlh wani lokacin bakida tausayi Asabe, duk irin kudin da kika samu yau, wanda rabon da ki rike irinsu harkin manta amma saboda dari 500 kinemi sama dan bawan Allah hawan jini. Asabe tace kinsanni akan kudi banida mutunci wlh, tunda harna iya kashe mazajena 2 saboda kudi, kinsan banida mutunci akan kudi, shiyasa bazan daga ma Zarah kafa akan kudi ba wlh, kina ganin sabida tsabar rowa dubu 2 tabamu duk irin wahalar damukasha, amma dayake biyan bukatar tane 150 taba boka. Dije tace ki kwantar da hankalinki, ai tunda de zata iya bada ko nawa ne ayimata aiki, mukam kakarmu ta yanke saka. Kinsan konawa boka yadauka yabamu sauran?  80 yadauka wlh, dariya Asabe tayi tace kai amma wannan boka yanada kirki, gaskiya naji dadi, dauko kibani kasona in adana.

Tunda Zarah ta isa gida wanka kawai tayi, taci abinci tawuce asibiti, lokacin dataje, har Hajjo ta farfado. Tea ta hada mata, takamata suka je bandaki. Seda tayi wanka tagyara jikinta sannan, Zarah tamika mata kayan da Alh, yakawo mata, sawa tayi tafito. Falak ce tashiga bandakin domin wanke kayan data cire.
   Bayan tasha tea taci abinci sannan tasha magungunanta. Zarah tace sannu Hajjo, Allah yabaki lfy, ya kuma kawo wani me amfani. Hajjo tace ameen. Zarah tajuya taga Falak bata nan, kuma Alh, yaje yin sallah. Tace amma Hajjo meze hana kibari sekin warke sosai sannan ki kara samun ciki, ina nufin kizo inraka ki gurin likitana asa maki robar hana daukar ciki, amma kada kibari Alh, yasani kinga seki huta sosai, daga baya se acire maki, nasan Alh, beda hkr ko baki warke ba, yana iya zuwa karbar hakkinshi, kinga niyanzu na huta. Hajjo takurama Zarah, ido harseda ta tsargu.
    Zarah tace kinyi shiru, murmushi tayi tace ai likita ma yace kozan kara samun ciki senan da shekaru sbd barin dana samu. Ajiyar zuciya Zarah tayi, batasan lokacin da murmushi ya kwace mata ba, tace wayyo gaskiya na tausaya maki, amma ai bakomai wata rana zaki samu. Kallonta kawai Hajjo takeyi, aranta tace ai idan mutum yanuna baya sonka daga farko, koyazo daga baya yace yana sonka kada kayarda dashi.

Segurin karfe 8 aka sallamesu. Bayan sunkoma gida, Alh, yace mairo tarika shiga tana taya Hajjo aiki kafin tasamu sauki. Zarah tace ai bakomai ma taje tayi mata sati 2 harta warke, Hajjo tace a,a Ummin Jalila ai za,a barki da aiki, idan tagama maki tunda nawa babu yawa setazo tamun. Alh, yace shikenan hakan ma yayi.

Tundaga wannan ranar Mairo take shiga part din Hajjo tana taya ta aiki, sosai mairo takejin dadin aiki agurin Hajjo, sbd tana da kirki, kuma bata kyamarta kamar Zarah, gashi tanayi mata alkhairi akai akai, harcewa takeyi dama Alh, yasamoma Zarah wata ita abarta anan, idan ta tuna aikin sati 2 kawai zatayi takoma can dazama batajin dadi, Sosai suke zama da Hajjo suyi ta fira, shiyasa ma seta gama aikin Zarah take tahowa gurin Hajjo. Duk wani labari na Hajjo babu wanda bata sani ba, sbd hakanan Hajjo taji mairo ta kwanta, mata gatade dattijuwa, amma tana bata girma, shiyasa ma bata iya kiranta da mairo sede tace mata Baba mairo, hakan bakaramin dadi yakema Mairo ba, Falak da Jalila ma haka suke cemata, amma banda Jidda.

Jidda ce kwance adakin saurayinta Al,amin, bayan sungama aikata masha,arsu, Al,amin yace Dear nah yakamata fa kitashi kiyi wanka inmaida ke gida, kinga ankusa tashi daga islamiyya, tunda nagama dora maki nawa karatun. Murmushi tayi tace wlh, dande Dady yana gari da anan zan kwana, banason tafiya inbarka. Al,amin yace nafiki son haka Jidda, shiyasa naso ace kinbari nazo gidanku muyi aurenmu mu huta kikace bakison aure yanzu. Jidda tace wlh, Al,amin rayuwar aure takura ce, duka yanzu shekarata nawa dazanyi aure, ai gara inbarai sena kai irin 27 ko 28 haka, yauwa lokacin nakara girma. Amma kawai yanzu da kuruciyata inshiga sahun manya. Murmushi Al,amin yayi yace shikenan ai nima bawai auren ne yadameni ba, tunda de inada kudi na nasan bazan rasa yan mata ba, duka Jidda ta kaimashi yana dariya yace, kemafa bani kadai kike kulawa ba, abinda nasani de nida ke muna son junanmu sosai, amma kowa yana kula duk wanda yasamu, ko kin manta da kaina ina hadaki da aboka naina masu kudi, kuma ni seki hanani kula wasu, aikinsan harakar bariki kowa yanada yanci. Jidda tace naji de amma aikasan kai na dabanne tunda kaine kafara sanina ,ya mace, yace wlh Jidda akanki nafara wannan sana,ar. Shiyasa nake bala,in sonki Jidda na. Murmushi tayi tace bara inyi wanka.

Haka rayuwarsu tacigaba datafiya, hanakalin Zarah bakaramin kwanciya yayi ba jin Hajjo bazata haihu yanzu ba, arizikin mijinsu sehabaka yakeyi, shiyasa yabiya ma Hajjo da Falak da su Jalila hajji, yace ma Zarah tabari tunda ita taje wata shekarar se sukara tafiya tare, baya son abrshi shi kadai. Bakaramin dadi taji ba, za,a barmata mijinta.

Lokacin da Mairo tacika sati 2 tana aiki agurin hajjo, ranar data dawo bangaren Zarah sallama takeyi amma jin shiru yasa tawuce dakin Zarah, taje zata kwan kwasa taji Zarah kamar tana waya, har zata juya taji Zarah tana dariya tana cewa, ai wlh, Inna Asabe, yanzu hankalina akwance yake, tunda mukayi nasarar zubar da waccan cikin na hajjo likita yace kozata kara haihuwa senan da shekaru, shiyasa nace dole inyima boka babbar kyauta sabida yabiyani, yanzu Alh, yabiya mata hajji ita da yara, harda wannan AGOLAR banzar akabiya mawa, narasa meyasa Alh, yake son maidata kamar kowa agidan nan. Ai kede kibari da sannu zankoresu subar gidan nan, toshikenan sekinjini. Mamaki ne yakama mairo jin abinda Zarah take fadi, saurin komawa tayi tanufi dakinta, tana tunanin hanyar dazata bi domin. Kare Hajjo daga sharrin Zarah.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/8, 4:02 PM] YAYA HAYAT: ???????????? AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ (  H,O,N,A)

Fita Mairo  tayi tashiga kitchen tacigaba da aikinta, tana tunanin maganganun Zarah, hakade ta barma cikinta, danbazata so afara jin wata magana abakinta ba, amma tayi alkawarin zata sa ido sosai aharkar Zarah, tunda tagano tacanza halinta.

Haka rayuwa tacigaba da tafiya, harsu Hajjo sunje hajji sundawo, sosai tayima Zarah da Baba mairo tsaraba, bayan kwana biyu suka shirya zuwa Abuja ita da Alh, domin kaima matar farouk abokin Alh, tsara barsu, dan bayan bikinsu akayima Faruok transfer yakoma can. Kwanansu 2 acan, bakaramin bacin rai Zarah tashiga ba, anyi tafiya banda ita.

Bayan dawowarsu, Mairo tashiga part din Hajjo, tana zuwa ta isketa abandakin falo tana ta amai, temaka mata tayi, bayan tagama suka dawo falo, mairo tace sannu Hajiya, amma inaganin kamar ciki ne dake ko? Hajjo tace nima haka nake tunani, dan tunkafin muje hajji nadena ganin al,ada ta, sede yaune nafara amai. Mairo tace aikinsan yanzu ba cikin farko bane, kila ma yayi wata 2 shiyasa baki fara laulayi dawuri ba.

Amma zankawo maki wani magani, inde kinsha zaki dena amai kuma zakiji kwarin jikinki. Hajjo tace aiko nagode Baba mairo, wlh bansan da abunda zan saka maki ba, Allah yasani nayi rashin uwa, amma gashi yanzu Allah yabani ke, inajinki tamkar uwata, babu abinda zan iya boye maki. Kwallan da mairo take boyewa suka zubo mata, Hajjo tace Baba mairo meyafaru kuma?  Mairo tace bakomai, kawai naji dadin kalamanki yata, tunda nake bantaba haihuwa ba, banida me kirana mana, segashi yau kinbani babban matsayi wanda bakowa ne yake amsa shiba. Hakika yau ina cikin farin ciki wanda. Nadade banji ba. Allah yayi maki albarka keda diyarki Falak.

Sede inaso infada maki wata magana, ada ina shakkun infada maki, sbd bansan yazaki daukeni ba, kila bazaki yarda da maganata ba. Amma ayanzu dakika bani matsayin uwa agareki, nasan zaki yarda da abunda zan fada maki, dan kinsan uwa bazata fadama yarta karya ba.

Inaso kiboye cikin dake jikinki har lokacin da zaki haifeshi, ko Alh, banaso kifada mashi kina da ciki harse yayi girma, nasan shi baza,a iya boyemashi ba. Hajjo tace meyasa kikace haka Baba mairo, nasan dole akwai dalilin dayasa kikace haka, dan Allah kifadamun koma menene, nayi maki alkawarin bazan bafadama kowa ba.

Anan mairo tafadama Hajjo duk abunda taji Zarah tana fadama Asabe awaya. Hajjo tagoge kwallan idonta, tace wlh jikina yabani Zarah ba sona take ba, kawaide tana yimun fuska 2, lokacin da aka kwantar dani asibiti take cemun wai inzo tarakani asakamun robar hana daukar ciki.

Anan jikina yabani wani mugun nufi take nufi dani, kawai sena fada mata likita yace kozan haihu senan da shekaru, wlh Baba mairo ina gama fada mata bakiga wani murmushi datayi ba. Tun daga nan nagane abinda take nufi dani.

Kuma insha Allah Zarah bazatasan ina da ciki ba sede taji haihuwa ta. Shima Alh, bazan fada mashi ba harse yayi kwari, shima sena rokeshi kada yabari kowa yaji, Mairo tace bara inje inkawo maki maganin.

Haka Hajjo tacigaba da renon cikinta babu wanda yasani daga mairo se Falak, su Jidda anyi graduation duk da bawani kokari tayi ajarabawarsu ba, su Falak kuma sunshiga ss3 karatu sukeyi sosai dan sunaso sucigaba da karatunsu idan sungama.

Jidda yanzu duk inda Al,amin zeje tare suke zuwa, ko da kwana nawa zeyi tunda Alh, baya zama gida yanzu sosai, Zarah kuwa tunda Jidda tana wadata ta da kudi babu abinda yadameta, abinda Jidda tagane ma Zariya tamaida gurin zuwanta, tunda taga Asabe bata kwaba mata duk inda taje kotayi dare bata cemata komai, kuma Baba bashida katabus agidan, hakan yasata yanzu tafi zama Zariya akan gidansu, koda Alh, yaji tana zuwa Zariya dadi yaji saboda yaga umminsu ita bata zuwa.

Lokacin da cikin Hajjo yacika wata 7 aranar Alh, yagane tana da ciki, yace lallai ma Hajjo yanzu nikike boyema abun farin ciki?  Dariya tayi tace wlh banso kagane ba, naso kawai kazo kaga jariri ko jaririya, shiyasa ko zanje awo nake cemaka zanje wankin kai. Amma kayafemun da karyar danayi maka. Jawota yayi yace bakomai, aikinsan dama ni ina baku damar fita duk lokacin da kukeso koda bana nan.

Amma gaskiya naji dadi sosai,  Allah yasa rayayyene, tace ameen. Amma dan Allah banaso kafadama Kowa har ummin Jalila, nafiso inbata mamaki tunda kai kaganoni.
    Yace shikenan angama daukarta yayi suka nufi daki.

Su Falak suna third term a ss3 Hajjo ta haifi yaronta me kyan gaske, babu wanda yasan tahaihu, dan cikin dare nafara nakuda kuma taci sa,a Alh, agurinta yake, haka suka hada kaya suka nufi asibiti, Falak kawai tasan suntafi, gurin karfe 8 suka dawo, bayan ya kaita part dinta yawuce part din Zarah, yanashiga yahadu da Mairo, yace tabar abinda takeyi taje Hajjo ta haihu, sosai mairo taji dadi, tace me aka haifa, yace namiji, barka tayi mashi sannan tawuce part dinsu.

Farin ciki kawai Alh, yakeyi, dakin su.  Jalila yaje yace tafito tacigaba da aikin da mairo takeyi, dan taje gurin Hajjo ta temaka mata ta haihu. Jalila cike da murna tace Dady meta haifa?  Yace kunsamu kani Jalila bakaramin dadi taji ba, fita tayi tawuce kitchen. Dakin Zarah yashiga, ganin yana cikin farin ciki ga bakinshi yaki rufuwa, tace Alh, yaude lafiya kake kamr wanda aka yima bushara da gidan, aljanna? Yace aidole kiganni haka, Hajjo ta haihu kuma tasami namiji me bala,in kama dani. Dariya Zarah tayi tace amafarkin yau ne kaga haka? Yace wlh da gaske nakeyi, tun dare muna asibiti. Zarah tace karbo yaron kukayi kome, nide nasan Hajjo bata da ciki. Ganin zata bata mashi lokaci yajata zuwa part din Hajjo.

Mutuwar tsaye Zarah tayi ganin Alh, yamiko mata yaro me bala,in kama dashi, kamar an tsaga kara, wata irin zufa ce tarika keto mata ta ko ina, tama rasa mezatayi, takasa karbar yaron, hawayene suka taho mata tayi saurin juyawa takoma. Falo, mamaki ne yakama Alh, ganin abinda Zarah tayi, amma su Hajjo sun harbo jirginta.

share please

0 comments:

Post a Comment